Shirin na Waiwaye Adon Tafiya, kan zo wa masu sauraro sau biyu a kowane mako, ranakun Assabar da yamma da lahadi da safe. Shiri ne da kan yi bitar muhimman labarai da rahotannin da aka gabatar a Sashen hausa na Rediyon Faransa RFI, inda mukan tantance mu zabo rahotannin da suka yi fice cikin mako.
A shirin na wannan mako, mun mayar da hankali ne kan labaran da suka fito daga Najeriya, Jamhuriyyar Nijar da wasu kasashen duniya. Amma shirin, ya faro ne da batun labarin wasan cin kofin Afrika da kasar Zambiya ta lashe sannan mun kammala da hira kan neman kiran taron kasa a tarayyar Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu