Isa ga babban shafi
UN

Tarihin sabon Sakatare Janar na MDD

Tsohon Firaministan kasar Portugal Antonio Guterres, na gab da darewa kan mukamin Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya bayan kasashe 15, mambobi a kwamitin tsaro na Majalisar sun jefa kuri’a a yau Laraba, in da ya zarce abokan takararsa wajen samun yawan kuri’u.

Sabon Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres
Sabon Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres REUTERS/Mike Segar
Talla

An haifi Guterres a ranar 30 ga watan Aprilun shekarar 1949 kuma ya rike mukamin Firaministan kasar Portugal daga shekarar 1995 zuwa 2002, bayan da ya shiga siyasa a shekarar 1976, a lokacin da aka gudanar da zaben demokradiya na farko a kasar bayan juyin juya halin da ya kawo karshen mulkin kama-karya na shekaru 50.

Gabanin darewarsa kan kujerar Firaminista a Guterres ya rike mukamin shugaban jam’iyyar ‘yan gurguzu.

A lokacin da yake shugabantar hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya tsakanin shekarar 2005-2015, jami’in ya jagorance ta wajen tinkarar matsalar ‘yan gudun hijira a kasashen Syria da Iraqi da Afghanistan.

A wancan lokacin dai, Gutteres bai yi kasa a gwiwa ba wajen yawan kiran kasashen Yamma da su zage dantse don taimaka wa ‘yan gudun hijira.

A yau ne dai mambobi 15 na kwamitin tsaro a Majalisar Dinkin Duniya suka zabe shi a matsayin sabon magatardan Majalisar bayan sun kada kuri’ar da ta bashi nasarar doke ‘yan takara guda 9 da suka hada da kwamishiniyar kasafi ta kungiyar tarayar Turai, Kristalina Georgieva ta Bulgaria.

A gobe ne dai za a gabatar da shi a zauren Majalisar don tattabar da zabensa a hukumance.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.