Afriaka ta kudu-Gabon
kasar Afrika ta kudu ta ce ba zata yiwa kasar Gabon Fin karfi ba dangane da Kungiyar AU
Shugaban kasar Africa ta kudu Jacob Zuma yace kasar sa ba zata yiwa kasar Gabon fin karfi ba wajen kokarin da suke yi na fidda sabon Shugaban Hukumar Kasashen Africa AU.Cikin watan Janairu na wannan shekarar dai Kasashen nahiyar sun kasa zaben Shugaban Hukumar Kungiyar tasu, tsakanin Shugaba mai ci Jean Ping wanda dan kasar Gabon ne dake rike da Mukamin tun 2008, da kumna ‘yar kasar Africa ta kudu Nkosa-zana, wadda kuma tsohuwar matar Shugaban Africa ta kudun ne.Koda a makon jiya Shugabannin nahiyar sunyi taro a kasar Benin domin duba lamarin, amma kuma bisa dukkan alamnu sai taro na gaba na kungiyar da zatayi a Malawi, cikin watan 7.
Wallafawa ranar: