Kamar yadda aka sani dai cutar SIDA, cuta ce mai karya garkuwar jiki kuma cuta ce da ke ci gaba da yaduwa tsakanin matasa maza da mafi yawan yara yaran mata. Cuta ce da wasu ma'aurata suka tsinci kansu da ita suka kuma amince da su ci gaba da rayuwar aurensu tare. To ko tana yiwuwa macce mai cutar SIDA ta samu juna biyu wato ciki ba tare da ta saka wa jaririnta ba ? Tambayar da likitoci suka amsa a cikin wannan shirin da cewa tana yiwuwa idan har maccen ta bi shawarar likitoci a cikin tsarin PTME tsarin nan na binciken harakar SIDA da kare da uwa. Na kuma samu macen da ta shaida da bakinta cewa a wurin awon ciki aka gane tana da cutar ta bi tsarin kuma ta haifi danta lafiya.
Sauran kashi-kashi
-
Bayani a kan cutar ƙyanda da yadda za a kare yara daga kamuwa
A wannan makon shirin zai yi duba kan cutar kyanda ko kuma measles a turance, cutar da galibi akan ga bullarta a irin wannan lokaci da ake fama da matsanancin zafi musamman a yankunan kasashen yammacin Afrika Sahel.13/05/202409:58 -
Yadda matasa ke rungumar tsarin yin kaho a zamanance
Shirin lafiya jari ce na wannan mako ya mayar da hankali ne kan tsarin yin kaho a zamanance06/05/202410:09 -
Karancin ruwa na haddasa tarin cutuka ga al'ummar arewacin Kamaru
Shirin Lafiya jari ce tare da Azima Bashir Aminu a wannan makon ya mayar da hankali ne kan yadda al’ummar yankin arewacin kamaru ke fuskanta matsalar rashin tsaftatacce kuma wadataccen ruwan sha ba, wanda ke haddasa gagarumar matsala ga lafiyar mazauna yankunan, wannan shi ne maudu’in da shirin na wannan mako zai mayar da hankali akai.03/05/202410:07 -
Yadda maza a Najeriya ba sa bai wa gwajin sankarar mafitsara mahimmanci
A wannan mako shirin ya mayar da hankali kan nau’ikan cutakan da ba a fiya mayar da hankali wajen yakarsu ba musamman a kasashe masu tasowa irin Najeriya, wannan nau’in cutuka kuwa sun kunshi kansar mafitsara ko kuma Prostate Cancer, nau’in kansar da ke matsayin mafi hadari ga maza, amma kuma ba ta samun kula duk da yadda ta ke kisan akalla mutum dubu 8 duk shekara a Najeriya.04/03/202410:00 -
Yawaitar gurbatattun jami'an lafiya a asibitocin Najeriya
A wannan makon shirin ya mayar da hankali kan yawaitar gurbatattun jami’an lafiya a asibitocin Najeriya wanda ke da nasaba da kodai rashin samun cikakken horo a kwalejojin lafiya ko kuma samun horon irin wadannan makarantu amma na bogi.A baya-bayan nan ana yawan ganin yadda ake bude tarin makarantu masu zaman kansu a sassan Najeriya da sunan horar da jami’an lafiya kama daga kwalejoji har da jami’o’I wadanda wasu daga cikinsu kan rasa sahalewar mahukuntan saboda rashin cancanta.29/01/202410:10