Mali
Dakarun kasar Mali sun kwace sansanin 'yan al-Qaeda
Gandun dajin Wagadu dake yankin arewa maso yammacin kasar Mali kusa ga kan iyakar kasar da Mauritanie, wanda ke fama da tashin hankali tun cikin watan jiya, na yan tsageran kungiyar Alka’ida reshen Mafhreb Islamiq Aqmi, a yau ya fada hannun dakarun sojan kasar Mali.Babban Kwamandan dakarun sojan kasar Mali a yankin Colonel Gaston Damango ya ce bisa yiyiwar dawowar yan tsageran, sun kara jan damara domin ganin yan alkaidar basu sake dawowa ba a guri.Tayiyu su dawo amma ina ganin Mu ne ya dace mu kara jan damara domin ganin basu sake dawowo ba.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: