Faransa
Majalisar Dokokin Faransa ta amince da matakin kan Libya
Majalisar dokokin kasar Fransa ta amince da gagarumin rinjaye, ci gaba da bada kudaden yakin da dakarun kasar keyi a Libya, bayan Prime Minista Francois Fillon ya ce, an kusa cimma yarjejeniyar siyasa.Bayan kwashe sa’oi uku ana tafka mahawara cikin majalisar wakilai, Ministan harkokin waje, Alain Juppe, ya ce jakadu sun shaida masa cewar, shugaba muammar Gaddafi na shirin sauka daga madafun iko.Prime Ministan ya shaidawa Yan Majalisun cewar, nan bada dadewa ba, za’a cimma yarjejeniyar siyasa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: