Tunisia
Fursunoni 71 Suka Mutu A Boren Tunisia
A kasar Tunisia fursunoni 71 ne suka rasa rayukan su sakamakon bore don kifar da Gwamnatin Zine El-Abidine Ben Ali.Ministan Sharia na kasar Lazhar Karoui Chebbi ne ya bada wadannan alkaluma.Ministan yace 48 daga cikin fursunonin gobara ta hallaka su a gidan yari dake Monastir.A yanzu haka dai kungiyoyin kodago a kasar nata taruwa a garin Sidi Bouzid inda aka fara yin bore a kasar.Kungiyoyin na kara neman jama’ar su dasu cigaba da bore Alhamis.
Wallafawa ranar: