Isa ga babban shafi
Tunisiya

Fira Minista Yayi Alkawarin Sauka Bayan Zabe

Fira Ministan  kasar Tunisia Mohammed Ghannouchi yayi alkawarin sauka daga mukamin ya daina siyasa kwata-kwata  bayan an gudanar da zabe karkashin tafarkin democradiyya  na farko  tun samun ‘yancin kasar daga kasar Faransa a shekara ta 1956.Fira Ministan ya fada cikin  wani shirin musamman na gidan Talabijin  na kasar cewa yayi alkawarin ganin ya jagoranci yin zabe na farko a kasar.Ya fadi cewa za'ayi zabukan wakilan majalisa dana Shugaban kasa cikin watanni shida masu zuwa.Fira Ministan wanda yake rike da wannan mukami tun lokacin da hambararren Shugaba Ben Ali  ya tsere makon jiya zuwa kasar Saudiyya, na wannan alkawari ne sakamakon kara boren gamagari, inda mutane ke neman dukkan wadanda sukayi zamani da tsohon Shugaban suyi bankwana da mulki. 

Fira Ministan Tunisiya Mohammed Ghannouchi
Fira Ministan Tunisiya Mohammed Ghannouchi rfi
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.