Hukumomin kasar Tunisiya Sun Tura Soja Muhimman Wurare
Hukumomin kasar Tunisiya sun tura Sojan kasar sassa birnin Tunis domin taimakawa maido da Doka da Oda, yankunan da jama'a ke cigaba da bore saboda rashin ayyukan yi da matsalar halin rayuwa.Wasu bayanai na cewa mutane akalla 50 ne suka gamu da ajalin su sakamakon wannan bore dan tsakanin nan.Motojin Soja na yaki sunyi ta sintiri titunan Tunis tun wayewar gari yau.An kuma tura Dakaru zuwa yammacin babban birnin kasar inda boren yafi kamari.Jiya masu bore sunyi ta jifan ‘Yan Sanda da duwatsu a yankin Ettadamen, inda aka kona motoci da damaWannan shine karo na farko da Hukumomin kasar suka tura sojoji domin kwantar da kura tun da aka fara wannan bore.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: