Mozambique
Ambaliya Da tsawa Sun Kashe Mutane 12 a Mozambique
A kasar Mozambik tsawa da ambaliyan ruwan sama sun hallaka mutane takwas a tsakiyar kasar wanda ya kawo yawan mamata 12.Kamar yadda jami'in ‘yan sanda na yankin, Belmiro Mutadiwa, yayi bayani, mamatan na wani taro ne karkashin wata bishiya, a yankin Mossurize dake gunduman Manica, dab da kan iyakan kasar da Zimbabwe, lokacin da tsawan ta sauka.Wani Jami'in Hukuma dake yankin yace ruwan saman da za'a samu nan da watanni biyu masu zuwa zai haifar da ambaliyan ruwan gaske a cikin kasar.
Wallafawa ranar: