Isa ga babban shafi

Sabuwar girgizar kasa ta sake afkawa gabashin Turkiyya

Wata sabuwar girgizar kasa mai karfin maki 5.6 ta sake afkawa yankin gabashin Turkiya yau litinin inda ta kashe mutum guda tare da jikkata dubbai baya ga rushe tarin gidaje.

Wani yanki da girgizar kasa ta afkawa a Turkiyya.
Wani yanki da girgizar kasa ta afkawa a Turkiyya. REUTERS - NIR ELIAS
Talla

Girgizar kasar ta yau litinin na zuwa ne kwanaki 7 bayan makamanciyarta da ta sake afkawa sassan kasar bayan mummunar girgizar kasar ranar 6 ga watan Fabarairu da ta kashe mutane kusan dubu 50 a kasar da makwabciyarta Syria.  

Sanarwar da hukumar kare afkuwar bala’o’I ta kasar ta fitar ta ce baya ga mutum guda da ya mutu akwai kuma wasu 69 da suka jikkata yayinda gidaje 29 suka rushe.

Hukumar ta ce jim kadan bayan afkuwar girgizar kasar, jami’anta suka isa yankunan da ibtila’in ya faru don kai dauki wannan dalili ne ya rage samun asarar rayuka.  

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.