Isa ga babban shafi
AFGHANISTAN-AMBALIYA

Ambaliyar Ruwan Sama ta kashe mutane 150 a Afghanistan

Akalla mutane 40 ne suka rasa rayukansu, a yayinda wasu kuma 150 suka bace, sakamakon ambaliyar ruwan saman da ta shafi  Arewacin kasar Afghanistan haka kuma arewa maso gabashin Kabul, babban birnin kasar. 

Ambaliyar ruwan sama ta mamaye birnin Kandahar na kasar Afghanistan.
Ambaliyar ruwan sama ta mamaye birnin Kandahar na kasar Afghanistan. JAVED TANVEER / AFP
Talla

Yanzu haka dai, ana ci gaba da gudanar da aikin ceton jama’a, domin samun damar ceto masu sauran numfashi  bayan saukar ruwan sama babu kakkautawa dake dauke da iska mai karfin gaske da ya mamaye gundumar Kamdesh da ke lardin Nuristan mai tazarar kilomita 200  arewa maso gabashin Kabul.

Bayanai da hukumomin kasar suka bayar sun nuna  cewa mutane dari da hamsin ne suka bata , a yayinda sama da gidajen zaman jama’a 80 suka rushe  sakamakon mummunar ambaliyar ruwan saman da ya  mamaye yankin.

A cewar mai Magana da yawun gwamnan Nuristan, wato saeed Momand, kawo yanzu sama da mutane 60 ambaliyar ruwa ta kashe a yankin.

A ko wace shekara dai saukar ruwan sama kamar da bakin kwarya na yin sanadiyar mutuwar daruruwan mutane a kasar ta Afghanistan.

Yanzu hada dai ana cike da fargabar cewa gidajen zaman jama’a da dama ne, galibi daga yankunan karkara ke kan rushewa sakamakon  rashin ingancin da suke da shi.

A bara dai mutane da dama ne suka rasa rayukansu  a sanadiyar  ambaliyar da ta biyo bayan saukar ruwan da ya mamaye yankunan lardin Parwan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.