Isa ga babban shafi
Amurka-India

Amurka ta yi barazanar sanya takunkuman Iran su shafi India

Amurka ta bukaci India ta yi karatun ta nustu game da alakar da ke tsakaninta da Iran, musamman kasancewarta babbar abokiyar cinikayyarta ta bangaren man fetur.Jakadar Amurkan a Majalisar Dinkin Duniya Nikki Haley ta ce kiran na a matsayin gargadi ga Indiyan a dai dai lokacin da Amurkan ke shirye-shiryen kakaba wasu sabbin takunkuman karya tattalain arziki kan duk wata kasa da ta ki yanke hulda da Iran.

Shugaban kasar Iran Hassan Rouhani tare da Firaministan India Narendra Modi yayin wata ganawarsu a Hyderabad da ke birnin New Delhi cikin watan Fabarairun 2018.
Shugaban kasar Iran Hassan Rouhani tare da Firaministan India Narendra Modi yayin wata ganawarsu a Hyderabad da ke birnin New Delhi cikin watan Fabarairun 2018. REUTERS/Adnan Abidi
Talla

Nikki Halley ta yi gargadin cewa sabbin takunkuman Amurkan na karya tattalin arziki da za su fara aiki ranar 4 ga watan Satumba ba za su yi rangwame kan duk wata kasa da ta yi kunnen kashi wajen kin yanke alakar kasuwanci da Iran ba.

India dai kusan ta la’akara da Iran ne wajen sayen galibin man fetur din da ta ke amfani da shi, inda Iran din ke matsayin kasa ta 3 da ke shigar da man fetur mafi yawa kasar ta India na akalla Yuro biliyan 1 da miliyan 25

Akwai dai kakkarfar dangantaka tsakanin India da Iran ko a baya lokacin da ta ke fama da takunkuman kasashe kafin cimma yarjejeniyar nukiliyarta a 2015.

A cewar Nikky Haley abu ne mai matukar wuya Indian ta iya sauya alakarta da Iran dare guda, amma shawara ce a gareta matukar ba ta bukatar takunkuman su shafe ta.

Nikki Haley ta ce za ta yi wata ganawa da Firaminista Narendra Modi na gaba kadan a birnin New Delhi don jan hankalinsa game da muhimmanci yanke huldarsu da Iran.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.