MDD na Daukan Matakan Hukunta Sojojin ta dake ayyukan Hashsha
Komitin Sulhu na MDD ya amince da wani kudiri dake bukatar janye ayarin sojan wanzar da zaman lafiya da aka sami wani soja a cikinsu da laifin zinace-zinace da ake samu dan tsakanin nan cikin sojojin dake ayyukan wanzar da zaman lafiya.
Wallafawa ranar:
Daftarin Dokan wanda kasar Amirka ke jagorantar ganin an aiwatar, wanda shine karo na farko da komitin sulhu na MDD ta dauka gameda batu na irin wadancan soja an amince da dokan, yayinda kasar Masar kawai taki nuna ra'ayin ta daga cikin su 14.
MDD ta nuna damuwa matuka yadda wasu sojan ta suka rika yaudaran ‘yan mata a kasar Janhuriyar Tsakiyar Africa, inda aka tura su aiki, suke bugewa da lalata da mata kawai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu