Isa ga babban shafi
Masar-Faransa

Masar da Faransa sun fara wani hadin gwiwar atisayen Soji

Kasashen Masar da Faransa sun fara wani hadin gwiwar atisayen soji tsakanin kasashen a gabar tekun Méditerranéen, inda kasar masar za tayi gwajin jiragen yakin nan na Rafale Fighter jets da ta siyo daga Faransa.

Jirgin yaki da Masar ta siyo daga Faransa
Jirgin yaki da Masar ta siyo daga Faransa AFP PHOTO / ECPAD
Talla

A tisayen da zai kwashe kwanaki ana yi zai gudana ne a gabar tekun Méditerranéen da ta ratsa garin Alexandria, a cewar dakarun masar.

Faransa dai ta ce zata shiga atisayen ne da jiragen ta samfurin Charles de Gaulle dake kaiwa mayakan IS hari a Syria da Iraqi, yayin da Rundunar sojin Masar tace jiragen ruwan yakin nan kirar Frigate da suma ta siya a Faransa za su shiga fagen.

A cewar ministan tsaro faransa atsisayen zai basu daman musayar dabarun fasahar yaki tunkarar ta’addanci.

A shekarar da ta gabata ne, Masar ta kula yarjejeniyar biliyoyin euro da Faransa wajen siyan jiragen yaki 24 wanda yanzu haka 6 sun isa kasar ta.

Atisayen kasashen biyu na zuwa yayin da kasashen yammacin ke cigaba da bayyana furgaban su dangane da karuwar mayakan IS a libya, kasar dake makawabtaka da Masar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.