Isa ga babban shafi

Tsare Imran Khan ya saba ka'ida - Kotun Kolin Pakistan

Tsohon Firaministan Pakistan Imran Khan da ke tsare  zai gurfana a gaban kotu wannan Jumma’a, bayan da kotun kolin kasar ta yanke hukuncin cewa kamen da aka yi masa ya a karshen mako wanda ya haifar da kazamin rikici tsakanin magoya bayansa da jami’an tsaro ya saba ka'ida.

Tsohon Franministan Pakistan Imran Khan, 04/11/22
Tsohon Franministan Pakistan Imran Khan, 04/11/22 AP - K.M. Chaudary
Talla

Alkalin kotun Umar Ata Bandial ya shaida wa Khan a wani zaman sauraren karar da aka yi a Islamabad babban birnin kasar ranar Alhamis cewa: Kamun da aka yi masa  bai dace ba, don haka dole a sake tsarin kamen.

An umurci Khan da ya ci gaba da zama a bayan kanta karkashin kariyar ‘yan sanda don kare lafiyarsa har zuwa yau Juma’a da za a bayyana a kotu.

Sake kama shi

Sai dai gwamnati ta sha alwashin sake kame Khan idan aka sake shi, lamarin da ake fargabar zai sake rura wutan rikici a kasar.

Tun bayan hambarar da shi daga mukaminsa a watan Afrilun da ya gabata, Khan ya gudanar da yakin neman zabe mai tsauri tare da yin suka da ba a taba ganin irinsa ba ga shugabannin Pakistan da manyan sojoji masu karfin fada aji.

Ya zarge su da shirya wani yunkurin kashe shi a watan Nuwamba da ya sa aka harbe shi a kafa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.