Isa ga babban shafi
Iran-Girgizar kasa

Girgizar kasa mai karfin maki 5.2 ta afkawa wani yanki na Iran

Girgizar kasa mai karfin maki 5.2 ta afkawa yankin arewa maso gabashin Iran a safiyar yau litinin, ko da ya ke zuwa yanzu babu cikakken bayani kan alkaluman mutanen da suka jikkata ko kuma barnar da girgizar kasar ta yiwa yankin.

Girgizar kasar ranar 13 ga watan Nuwamban 2017 da yankin Sarpol-e Zahab na Irán ya fuskanta.
Girgizar kasar ranar 13 ga watan Nuwamban 2017 da yankin Sarpol-e Zahab na Irán ya fuskanta. REUTERS/Tasnim News Agency
Talla

Mahukuntan Iran sun ce da misalin karfe 8:32 na safiyar yau ne girgizar kasar ta afkawa wani yanki da ke gab da birnin Quchan a lardin Razavi Khorasan wadda ya mamayi wurin da fadinsa ya kai kilomita 6.

A cewar Mahukuntan girgizar kasar ta shafi wani yanki na babban birnin lardin Mashhad da ke gab da iyakar Iran da Turkmenistan, birnin na biyu mafi girma a kasar.

Kungiyar agaji ta Red Cresent ta ce jami’anta na cikin shirin ko ta kwana don tunkarar duk wani kalubale da girgizar kasar ka iya haifarwa a yankin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.