Dubban Manoma a India sun gudanar da zanga-zanga
A kasar India dubunnan manoma sun yi zanga -zanga a kusa da babban birnin New Delhi a wannan Lahadi, inda suka sha alwashin ci gaba da bijirewa gwamnati kan dokokin aikin noma da ake cece kuce da suke ganin za su lalata rayuwarsu.
Wallafawa ranar:
Masu zanga-zangar da suka kunshi Maza da Mata sunyi ta rera taken "manoma, Leburori da kuma haɗin kai!", dauke da tutocin ƙungiyar manoma ta ƙasa a gundumar Muzaffarnagar ta jihar Uttar Pradesh.
Manoma sun yi sansani a kan iyakokin Delhi tun daga ƙarshen watan Nuwamba lamarin da ke zama cikin manyan ƙalubalen gwamnatin Firayminista Narendra Modi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu