Daukacin ma'aikata 53 na jirgin ruwan Indonesia da ya bace sun mutu
Rundunar sojin Indonesia ta sanar a Lahadin nan cewa dukkanin ma’aikatan jirgin ruwan karkashin ruwan nan nata da ya bace a makon da ya gabata sun mutu, jim kadan bayan da ta tabbatar da cewa an gano tarkacen jirgin a gabar ruwa.
Wallafawa ranar:
Hukumomi sun ce da sanyi safiyar Lahadin nan ne suka hango wasu alamu daga wani bangaren tekun Bali mai zurfin mita 800, wato fiye da iya zurfin da jirgin KRI Nanggala 402 zai iya jurewa.
Wanna na zuwa ne bayan da sojin ruwan kasar ta Indonesia suka tabbatar da cewa sun gano karikitan jirgin, sun a mai ayyana cewa nutsewa jirgin ya yi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu