Mu na maraba da duk wata tattaunawa tsakaninmu da Saudiya- Iran
Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta ce kasar a shirye ta ke kuma tana maraba da duk wata tattaunawa tsakaninta da Saudiya, duk da tsamin alakar da ke tsakaninsu kusan shekaru 6 da ya kai ga yanke hulda.
Wallafawa ranar:
Kakakin ma'aikatar Saeed Khatibzadeh yayin zantawarsa da jaridar Financial Times ya ce a kowanne lokaci Iran na farin cikin tattaunawa da Saudi Arabia, dai dai lokacin da jita-jitar ganawa tsakanin wakilan bangarorin biyu ke ci gaba da karade kafofin yada labarai.
Sai dai Saeed Khatibzadeh ya ki amsa tambayar gaskiyar batun ganawar bangarorin biyu a Iraqi da nufin gyara alakar da ke tsakanin kasashen biyu wadda ta wargaje tun a 2016, inda ya ce ita kanta Iran ta samu labarin ne a jaridun Duniya.
Kasashen biyu dai na banbancin akida a muhimman al'amuran da suka shafi gabas ta tsakiya ciki har da rikicin kasar Yemen inda Iran ke goyon bayan 'yan tawaye a bangare guda Saudiya ke goyon bayan gwamnatin hadin kan kasar.
A cewar Khatibzadeh Iran na goyon bayan tattaunawa tsakaninta da babbar abokiyar gabar ta ta Saudiya la'akari da yadda sulhu tsakaninsu zai amfani al'ummomin kasashen biyu haka zalika zai daidaita al'amura a gabas ta tsakiya.
Wasu majiyoyi sun bayyana cewa kasashen biyu sun faro tattaunawa a Iraqi ne kan batun yakin kasar Yemen wanda kuma bayanai ke cewa da yiwuwar samun nasara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu