Dubban 'yan Isra'ila na zanga-zangar neman Netanyahu ya yi murabus
Dubban ‘yan Isra’ila sun sake fita kan titunan birnin Kudus, inda suke zanga-zangar neman murabus din Firaministan kasar Benjamin Netanyahu, bisa zarginsa da laifukan rashawa, da kuma gaza daukar matakan dakile yaduwar annobar coronavirus.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce tun cikin daren ranar asabar, aka soma samun arrangama tsakanin masu zanga-zangar da jami’an tsaro, lamarin da ya cigaba zuwa wayewar garin yau lahadi, a gaf da gidan Firaminista Netanyahu.
Mako na 8 kenan da dubban ‘yan Isra’ila ke gudanar da zanga-zangar ta kin jinin Netanyahu.
Hotunan da aka wallafa a shafukan Internet sun nuna yadda ‘yan sanda ke jan masu zanga-zangar da suka damke, bayan hana su yin tattaki zuwa cikin harabar Firaministan na Isra’ila.
Jaridar Haaretz dake kasar tace yawan masu zanga-zangar da suka fita a biranen kasar ranar Asabar, ya kai dubu 50.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu