Isa ga babban shafi
Saudiya

Jirgin yakin Saudiya ya yi hatsari a Yemen

Wani jirgin yaki mallakin rundunar hadakar da Saudiya ke jagoranta a Yemen, ya yi hatsari a arewacin lardin al-Jawf.

Saudiya ba ta yi bayani kan asarar rayuka a hatsarin jirgin yakinta ba a Yemen
Saudiya ba ta yi bayani kan asarar rayuka a hatsarin jirgin yakinta ba a Yemen FAYEZ NURELDINE / AFP
Talla

Mai magana da yawun rundunar hadakar da ke yaki da ‘yan tawayen Houthi na Yemen, ya tabbatar da aukuwar hatsarin jirgin a daidai lokacin da yake kan gudanar da aiknsa.

Saudiya ba ta yi bayani ba game da rasa rai ko kumma jikkata a wannan hatsarin jirgin da i mayakan Houthi suka ce, su suka kakkabo shi.

A bangare guda Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, fararen hula 31 aka kashe a wani harin sama da Saudiya ta kaddamar a jiya Asabar a lardin al-Jawf.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.