Isa ga babban shafi
Syria-Rasha

EU ta bukaci gaggauta tsagaita wuta a Syria

Kungiyar kasashen Turai EU, ta ce ya zama dole gwamnatin Syria da kawayenta su kawo karshen barin wutar da suke yi kan ‘yan tawaye, da wasu kungiyoyin ‘yan ta’adda a lardin Idlib, abinda yayi sanadin halakar fararen hula da dama, da kuma tagayyara wasu dubbai.

Wasu yankuna da sojin Syria suka yiwa luguden wuta a yankin Idlib.
Wasu yankuna da sojin Syria suka yiwa luguden wuta a yankin Idlib. Delil SOULEIMAN / AFP
Talla

Ministan harkokin waje na kungiyar Tarayyar Turan Josep Borrell da ke wannan kira ya kuma dora alhakin hasarar rayukan daruruwan fararen hula a lardin kan gwamnatin Syria da Rasha.

A farkon watan Disambar nan kawancen dakarun Syria da Rasha suka kaddamar da sabon farmaki kan lardin na Idlib a arewacin kasar ta Syria, dake zama tungar karshe ta ‘yan tawayen kasar, duk da yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma tsakanin bangarorin a watan Agustan da ya gabata.

Wata kiddidiga da majalisar dinkin duniya ta fitar a baya bayan nan ta nuna cewar, a tsakanin 12 ga Disambar da muke zuwa 25 ga watan, luguden wutar dakarun na Syria da Rasha kan ‘yan tawaye, ya tilastawa fararen hula sama da dubu 2 da 35 tserewa daga muhallansu.

Wannan tasa a jiya lahadi kungiyar kasashen Turai ta bukaci kaiwa ‘yan gudun hijira akalla miliyan uku da har yanzu ke lardin na Idlib agajin gaggawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.