Isa ga babban shafi
China-Korea ta Arewa

Kasashen China Japan da Korea ta kudu na taro kan Korea ta Arewa

Kasashen China Japan da Korea ta kudu na wani taron hadin gwiwa da China ke karbar bakonci yau Talata, taron da ke da nufin hadin kan kasashen dama yadda za su bullowa makwabciyarsu Korea ta Arewa.

Shugaba Kim Jong-un na Korea ta Arewa.
Shugaba Kim Jong-un na Korea ta Arewa. KCNA VIA KNS / AFP
Talla

Taron wanda ke gudana a birnin Chengdu na kudu maso yammacin China na zuwa ne a daidai lokacin da wa’adin alkawarin kyautar Kiristimeti da shugaban Korea ta Arewa Kim Jong Un ya yi ke daf da cika, wanda yasa ake ganin taron na da nasaba da kalaman na Kim Jong Un.

Kasashen 3 dai wadanda ke matsayin makusanta ga Korea ta Arewa musamman China da ake kallo a matsayin uwar gijiyarta, kalaman na Kim tun cikin watan jiya ya tayar da hankulansu bisa tsoron kada alkawarin ya zamo karkashin shirin kasar ne na makaman nukiliya.

Kim Jong Un, a tun daga bara suka fara dasawa da Donald Trump na Amurka, ya yi alkawarin bayar da kyautar Kristimati, kyautar da bai fayyace abin da ta kunsa ba, ko da dai masharhanta na ganin ba zai wuce wani sabon gwajin makamin nukiliya ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.