Mayakan ISIS da dama sun mika kansu a Syria
Hukumomin da ke sa ido kan yakin Syria, sun ce mayakan kungiyar ISIS masu yawa sun mika kansu, ga rundunar Kurdawan YPG da Amurka ke marawa baya.
Wallafawa ranar:
Yawan mayakan na ISIS da suka zubar da makamansu ya kai 200, ya biyo bayan gagarumin farmakin da mayakan Kurdawan suka kaddamar kan kauyen Baghouz, yanki mafi fadi na karshe da ke karkashin ikon ISIS a Syria.
Mayakan na ISIS sun samu damar mika kansu ne, bayan da rundunar hadaka ta ‘yan tawayen Syria da mayakan Kurdawa suka sassauta hare-haren da suka kaddamar akansu, domin baiwa fararen hula damar ficewa daga yankin.
Har yanzu dai babu karin bayani kan yawan mayakan na ISIS da suka rage a cikin kauyen na Baghouz.
Duk da cewa ana gaf da murkushe ISIS a kasashen Syria da Iraqi, masana fannin tsaro sun bayyana cewa har yanzu mayakan kungiyar suna da sauran barazana, la’akari da hare-haren kunar bakin waken da suke kaiwa a manyan birane da kauyuka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu