China zata afkawa Taiwan
Shugaban China Xi Jinping a fusace ya gargadi hukumomin Taiwan da su sake manufa tareda mika wuya zuwa kasar China don kasancewa kasa daya.
Wallafawa ranar:
Shugaban China a yayinda yake ganawa da membobin gwamnatin China ya jaddada cewa indan ta kama China zata yi amfani da karfin soji wajen sake dawo da Taiwan karkashin ikon ta.
A shekara ta 2017 dai ne shugabannin kasashen China da Taiwan suka gana da juna a karon farko tun yakin basasa da ya raba kasashen biyu, shekaru sama da 67. Shugaban China XI Jinping da takwaransa na Taiwan Ma Ying-jeou sun gama hannu na tsawon sama da minti guda, ala’amarin da ba a zaci zai faru ba a haduwar shugabannin biyu.
Shugabannin sun yi murmushi a lokacin da suke gaisawa da juna a gaban ‘yan jaridu.
Wannan dai ne karon farko da Shugabannin bangarorin biyu suka hadu tun ballewar Taiwan daga China a 1949.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu