Isa ga babban shafi
Falasdinu

Falasdinawa sun kaddamar da gangami akan iyakar Isra'ila

Daruruwan Falasdinawa a yankin Gaza sun kafa tantuna akan iyakar yankin da Isra’ila, yayin shirin kaddamar da gagarumin gangami na nuna bacin ransu kan Isra’ila, na tsahon makonni 6.

wasu daga cikin tantunan da matasan Falasdinawa suka kafa a yankin zirin Gaza, yayin shirin zanga-zangar Lumana ta nuna bacin rai kan takurar Isra'ila.
wasu daga cikin tantunan da matasan Falasdinawa suka kafa a yankin zirin Gaza, yayin shirin zanga-zangar Lumana ta nuna bacin rai kan takurar Isra'ila. AP
Talla

Sai dai kuma ana fargabar komai ka iya faruwa tsakanin su da Sojin Isra’ila da suka ja daga

Falasdiwan da ke samun goyon bayan kungiyar Hamas, na cigaba da tsayawa kai da fata wajen kafa tantunan, a dai dai lokacin da ake cigaba kallon kallo, tsakanin su da sojin Isra’ila

Koda yake dai masu shirya gangamin sun ce na lumana ne, Isra’ila tace akwai fargabar fakewa ne da guzuma don harbin karsana.

Kawo yanzu dai Falasdinawa biyar aka harbe, yayinda suka hari iyakar Isra’ila, kamar yadda ma’aikatar lafiyar Falsdinun ta tabbatar.

Lamarin dai na zuwa ne a dai dai lokacin da Amurka ke kokarin tabbatar da ofishin jakadancinta a birnin Kudus, abinda Palasdinawan suka bayyana da ranar masifa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.