Isa ga babban shafi
Yemen

Rayuka sun salwanta yayin rikici tsakanin ƴan-bindiga a Yemen

Rahotanni daga birninn Aden da ke yammacin ƙasar Yemen sun tabbatar da cewa mutane da dama sun rasa rayukansu wasu kuma sun samu raunuka lokacin da aka yi artabu tsakanin ƙungiyoyin ƴan-bindiga.

Garin Aden na kudancin Yemen.
Garin Aden na kudancin Yemen. STRINGER / AFP
Talla

Mazauna birnin sun ce ƙungiyoyin ƴan-bindiga biyu da ke da mabiya watse a unguwanni daban-daban ne suka yi musayar wuta tsakanin su a ranar Lahadi.

Wannan rikici ya zo ne bayan ƙarewar wa'adin da ƴan adawa suka bai wa gwamnatin ƙasar na ajiye mulki a ranar Lahadi.

Gwamnatin dai na iko ne da kimanin kashi 4 cikin 5 na ƙasar, sai dai yan tawaye a Aden na yunƙurin farfado da zancen cin-gashin-kai na yammacin ƙasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.