Isa ga babban shafi
Koriya

Koriya ta kudu ta gabatar da tsarin tattaunawa da ta Arewa

Kasar Korea ta Kudu ta fitar da wani tsarin tattaunawar sulhu da makwabciyarta Korea ta Arewa a ranar 9 ga wannan wata na Janairu.

Shugaban kasar Koriya ta Kudu Moon Jae-In
Shugaban kasar Koriya ta Kudu Moon Jae-In AFP
Talla

Tattaunawar da ke biyo bayan tayin da shugaban Korea ta Arewa Kim Jong-Un ya gabatar a jawabansa na shiga sabuwar shekara da ke cewa, kasar na bukatar halartan gasar wasannin Olypmics da ke tafe.

Ministan hadin-kan kasar Korea ta Kudu Cho Myoung-Gyon ya fadawa taron manema labarai cewa ana sa ran tawagar kasashen biyu su zauna gaba-da-gaba domin tattaunawa.

Kasashen biyu da basa ga maciji tun kawo karshan yakin koriya a shekara ta 1950 zuwa 1953, rabonsu da zaman tattaunawa tun a cikin shekara ta 2015.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.