Isa ga babban shafi
Afghanistan

NATO ta ce Amurka ta jikkata mutane a Kabul

Kungiyar Kawancen tsaro ta NATO ta ce wasu jerin hare-haren saman da Amurka ta kai Kabul da ke Afghanistan sun yi sanadiyar jikkata mutane da dama.

Dakarun NATO a birnin Kabul na Afghanistan
Dakarun NATO a birnin Kabul na Afghanistan REUTERS/Mohammad Ismail
Talla

Sanarwar da kungiyar ta bayar ya nuna cewar an kai hare-haren ne kan wasu mutane da ake zargin 'yan ta’adda ne lokacin da suka harba makamin roka jin kadan bayan saukar Sakataren Tsaron Amurka Jim Mattis a Kabul.

Ma’aikatar cikin gidan Afghanistan ta ce mutun guda ya mutu yayin da 11 suka jikkata.

Kungiyar Taliban da mayakan ISIS sun dauki alhakin harba makamin rokar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.