Isa ga babban shafi
Korea ta Arewa

Korea ta Arewa ta sake harba makamai masu linzami

Kasar Korea ta Arewa ta sake harba makamai masu linzami zuwa gabar tekun da ke gabashinta, dai dai lokacin da sojin Amurka da na Korea ta Kudu ke gudanar da atasaye, wanda Korea ta Arewa ta bayyana shi a matsayin tsokanar yaki daga bangaren kasashen biyu.

Wani katafaren majigi a birnin Tokyo na kasar Japan da ke nuna yadda korea ta Arewa ta harba daya daga cikin makamai masu linzamin da ta gwajinsu a cikin watan Agusta, shekarar 2017.
Wani katafaren majigi a birnin Tokyo na kasar Japan da ke nuna yadda korea ta Arewa ta harba daya daga cikin makamai masu linzamin da ta gwajinsu a cikin watan Agusta, shekarar 2017. REUTERS/Toru Hanai
Talla

Sai dai cikin sanarwar da ta fitar, rundunar sojin Amurka, ta ce, Korea ta Arewan bata samu nasarar gwajin makamai masu linzamin uku ba, masu cin gajeren zango.

Makami na farko dai ya tarwatse ana harba shi, yayinda sauran guda biyun suka gaza yin nisan da ake bukata, inda sukai tafiyar kilomita 250 kawai zuwa cikin teku.

Amurka ta ce gwajin makaman bai yi wata barazana ga rundunar ta ba da ke tsibirin Guam, inda a farkon watan da muke ciki Korea ta Arewa ta yi barazanar kai wa hari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.