Isa ga babban shafi
Iraqi

Mosul: Tsugunno bata karewa fararen hula ba

A daidai lokacin da rundunar sojin kasar Iraki ke cewa ta kama sama da kashi biyu cikin uku na birnin Mosul, wanda ake kallo a matsayin babbar cibiyar ga kungiyar ISIS ko kuma Daesh, jama’a da dama, da yakin ya rutsa da su, ke fama da matsaloli musamman a bangaren kiwon lafiya.

Fararen da suka tsere daga muhallansu dalillin yakin da sojin Iraki ke gwabzawa da mayakan IS a yammacin birnin Mosul.
Fararen da suka tsere daga muhallansu dalillin yakin da sojin Iraki ke gwabzawa da mayakan IS a yammacin birnin Mosul. REUTERS
Talla

Philippe de Vaillant, babban jami’in kungiyar agajin kiwon lafiya ta Medecins Sans Frontieres, wato kungiyar likitoci ta kasa da kasa, ya ce matsalar ta kara kamari musamman a cikin wannan wata na Yuni.

Jami’in ya ce, babban kalubalen shi ne, mutane ba sa iya isa ga cibiyoyin kiwon lafiya, musamman a cikin ‘yan watannin baya-bayan nan, kuma matsalar ta fi shafar kananan yara da kuma masu manyan shekaru.

Zalika idan aka dauki jariran da ake haihuwa a ‘yan watannin nan, mafi yawansu ba su taba samun kulawar wani jami’in kiwon lafiya ba, kuma haka matsalar take a bangaren aikin tiyata, ko cire wa jama’a harsasai da dai sauransu.

A cewar Philippe de Vaillant, akwai wadanda suka share tsawon makwanni da raunuka a jikinsu, ba tare da sun samu isa ga wani jami’in kiwon lafiya domin taimaka masu ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.