Isa ga babban shafi
Iraqi

Dakarun Iraqi na ci gaba da kutsa kai Mosul

Yau ranar ta biyu dakarun Iraqi na sake nausa kai Mosul, yayin da Majalisar Dinkin Duniya ke sake bayyana furgaba game da makomar fararen hula sama da miliyan daya da rabi da ke rayuwa a birnin na Iraqi, a gaggarumin farmaki kwato yankin daga hannu mayakan IS.

Dakarun iraqi da taimakon mayakan Kurdawa na fafutukar kwato Mosul daga ISIS
Dakarun iraqi da taimakon mayakan Kurdawa na fafutukar kwato Mosul daga ISIS REUTERS/Azad Lashkari
Talla

Wani babban jami’in Majalisar ya yi gargadi samun Karin miliyoyin ‘yan gudun hijira sakamakon wannan farmaki.

A cewar Jami’in, Lise Grande, kamar yadda suka samu bayanai nan da kwanaki 5 zuwa 6 za a samu daruruwan ‘yan gudun hijira da ke neman tsira daga Mosul.

Tun a shekarar 2014 IS ke iko da Mosul, sai dai dakarun na Iraqi da taimakon rundunar kawance Amurka, na samun gallaba kan mayakan a hare hare sama da ake kai wa cikin garin.

Shugaban kasar Turkiya, Recep tayyib Erdogan, ya ce kasarsa za ta bayar da gudunmawa a yakin, inda ya ce wanann yaki ba wanda Ankara za ta zura ido ba ne.

Kungiyar IS da ke kokarin kafa daularta a Syria da Iraqi na fusknatar koma baya a ayyukan ta na jihadi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.