Isa ga babban shafi
Syria

Syria ta hanawa ‘Yan tawaye bude hanyar Aleppo

Rahotanni daga Syria sun ce dakarun gwamnatin Bashar Al Assad sun kashe ‘Yan tawaye akalla 29 a yayin da ‘Yan tawayen ke kokarin bude wata hanyar shigar masu da kaya a yankin Aleppo.

Mayakan da ke biyayya ga Dakarun gwamnatin Bashar al Assad na Syria
Mayakan da ke biyayya ga Dakarun gwamnatin Bashar al Assad na Syria REUTERS/Rodi Said
Talla

Kungiyar da ke sa ido a rikicin na Syria tace ‘Yan tawayen da aka kashe sun kunshi na kungiyar mayakan Faylaq al Sham da na mayakan al Nusra mai alaka da Al Qaeda.

Sai dai babu wani cikakken bayani akan adadin sojojin gwamnati da aka kashe a fadan da aka gwabza a yankin na Aleppo a yau Lahadi.

Rahotanni sun ce farmakin na dakarun gwamnati ya haramtawa ‘Yan tawayen bude hanyar a Aleppo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.