An kashe masu aikin Polio a Pakistan
Mayakan Taliban sun kai hari tare da hallaka ‘yan sanda 7 dake aikin tsare jami’an lafiya a yayin da suke baiwa yara riga kafin Polio a birnin Karachi dake Pakistan.
Wallafawa ranar:
A baya mayakan sun shahara wajen kai hari kan jami’an kiwon lafiya don adawar da suke da yaki da cutar Polio, sai dai kuma a baya bayanann mayakan Taliban sun koma kai harin akan jami’an tsaro dake aikin kare su.
Bayan aukuwar lamarin kungiyar Taliban reshen Pakistan ta dauki alhakin kai harin na yau.
Pakistan na daga cikin kasashen duniya da ake da yawan alkaluma na yara da cutar Polio ke hallakawa duk shekara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu