Isa ga babban shafi
Koriya ta Kudu-Koriya ta Arewa

Korea ta Kudu da ta Arewa sun gana akan sabaninsu

Kasashen Korea ta Kudu da Korea ta Arewa sun gudanar da wata tattaunawa da nufin cimma matsaya akan tankiyar da ke tsakaninsu game da kan iyakokinsu, al-amarin da ya kusan haifar da yaki a tsakaninsu.

Wakilan kasashen biyu Hwang Boo-Gi na Korea ta Kudu da Jon Jong Su na Korea ta Arewa a zamansu na yau.
Wakilan kasashen biyu Hwang Boo-Gi na Korea ta Kudu da Jon Jong Su na Korea ta Arewa a zamansu na yau. Reuters/路透社
Talla

Duk da dai ana fatan duk wata tattaunawa a tsakanin kasashen biyu za ta taka rawar gani, amma lura da zaman da suka gudanar a baya, mawuyaci ne su cimma matsaya mai dorewa.

Kusan shekaru biyu kenan da suka gudanar da irin wannan zaman da nufin zantawa kan jerin batutuwan da suka shafe su, yayin da suka dau shekaru da dama suna takun tsaka da juna.

Shugaban wakilan Korea ta Kudu Hwang Boo-Gi ya fada wa takwaransa na Korea ta Arewa Jon Jong-Su cewa, ya kamata su taka gagarumar rawa wajan samar da hanyoyin inganta hulda a tsakaninsu kuma ya yi fatan za su magance jerin matsalolinsu daya bayan daya.

A ganawarsu ta farko a safiyar yau jumma’ kasashen biyu sun shafe tsawon minti talatin, inda wakilan bangaorin biyu suka bayyana shirinsu na kawo karshen tankiyar amma daga bisani sun sake dawo wa a maraicen yau domin ci gaba zaman, kuma sun dau tsawon lokaci suna ganawa.

Zaman na yau dai na zuwa ne kwana guda da sanawar da shugaban Korea ta Arewa Kim Jong-Um ya fitar, inda ya ce, kasarsa ta kirkiri wani Bam daga makamashin Nukliya, lamarin da jefa shakku a zukatan Amurka da Korea ta Kudu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.