Taliban ta kafa tuta a Kunduz
Mayakan Kungiyar Taliban sun kaddamar da farmaki a lardin Arewacin birnin Kunduz dake kasar Afghanistan tare da kafa tutarsu a wani dandali.
Wallafawa ranar:
Daruruwan mayakan kungiyar ne suka kai farmakin a safiyar yau a birnin na Kunduz wanda suka samu damar shiga daga hanyaoyi uku yayin da aka tura Jami’an 'Yan Sandan Afghanistan zuwa birnin domin fafatawa da Mayakan.
Wasu jami’an tsaro sun ce Mayakan sun yi nasarar fasa gidan yarin Kundiz, inda suka kubutar da 'yan uwansu, kana sun karbe ikon wani asibiti dake cikin birnin.
An dai samu hasarar rayuka da dama da suka hada da Jami'an 'Yan Sanda yayin da wasu kuwa suka jikkta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu