Kurdawa na samun nasara a kan mayakan ISIS a Syria
Dubban yan gudun hijira na ci gaba da tserewa fadan da ake tabkawa tsakanin Kurdawa da mayakan Jihadin kungiyar Isis a kasar Syriya al'amarin da ya haifar da kwararar 'yan gudun hijira a kasar Turkiya.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Yanzu haka mayakan Kuradawa a kasar Syriya na ci gaba da dannawa zuwa garin Tal Abyad dake rike ga hannu mayakan jihadin islamar kungiyar Isis a kasar Syriya, al’amarin da ya haifar da kwararar yan gudun hijira a kasar Turkiya mai makwabtaka da yankin.
Tuni dai shugaban kasar ta Turkiya Recep Tayyip Erdogan a yau lahadi ya bayyana damuwarsa dangane da kwararar yan gudun hijirar a cikin kasarsa, sakamakon farmakin da mayakan kurdawan ke kaiwa, al’amarin da yace babbar baraza na ce ga kasarsa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu