Isa ga babban shafi
China

Babu wanda ya tsira a hatsarin jirgin ruwan China

Jami’an gwamnatin kasar Sin sun ce zai yi wuya a sami wanda ya tsira da ransa a hatsarin jirgin ruwan da ya nutse da masu yawon bude ido sama da 400. An tabbatarwa ‘yan uwan wadanda ke cikin jirgin ruwan hakan ne, bayan da aka tsamo jirgin da ya nutse da kusan mutane 460, a ranar litinin da ta gabata.

Hukumomin China na ci gaba da aikin lalaben jirgin da ya nutse a teku.
Hukumomin China na ci gaba da aikin lalaben jirgin da ya nutse a teku. Reuters
Talla

Zuwa yanzu mutane 14 ne kawai suka tsira daga hatsarin, kuma an sami gawarwakin wasu kusan 100 amma daruruwa ne suka bata.

Ana hasashen mutane 442 suka mutu ko suka salwanta, al’amarin da aka danganta mafi muni a tsawon shekaru 70 a China.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.