Isa ga babban shafi
Malaysia

Sojojin ruwan Malaysia za su ceto bakin haure

Firaministan Malaysia Najib Razak ya bai wa rundunar sojan ruwan kasar umarnin n ceto wasu kwale kwalen da ke dauke da bakin haure da suka hada da ‘yan kabilar Rohingya daga kasar Myanmar. Cikin sanarwar da ya sanya a shafin shi na Facebook, Najib yace dole a kaucewa hasarar rai, a daidai lokacin da ake fargabar bakin hauren sun makale a kan teku.

Kwale Kwale dauke da 'yan kabilar Rohingya da 'yan Bangladesh a tekun Julok, lardin Aceh a Indonesia
Kwale Kwale dauke da 'yan kabilar Rohingya da 'yan Bangladesh a tekun Julok, lardin Aceh a Indonesia REUTERS/Syifa/Antara Foto
Talla

Hakan na nunayanzu Malaysia za ta shiga aikin neman kwale kwalen bakin hauren da suka bace.

Wannan kuma na zuwa ne a daidai lokacin da wakilai daga Amurka, da sauran kasashen kudu maso gabashin Asiya suka nufi kasar, don tattauna matsalar bakin haure.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.