yawan mutanen da suka rasa rayukansu a girgizar kasar Nepal sun haura dubu 6
Sakamakon Alkaluman yazan mutanen da suka rasa rayukansu a cikin girgizan kasar data afkawa kasar Nepals a zannan makon sun kai 6,204, yayinda har yanzu ake nasarar kara zaro mutane da suka makale a karkashin kurakuzan gine-ginen da suka rushe.
Wallafawa ranar:
A jiya alhamis a birnin Kathmandu an yi nasarar ceto mutane biyu a karkashin gine-ginen da rayukansu, alamarin daya karawa masu aikin ceto karfin guiwar cewa ana iya samun Karin wasu mutanen da sauran numfashi.
Masu aikin ceto daga kasashen duniya sama da 20 ke taimakawa wajen gudanar da ayukan ceton bayan abkuzar mummunar girgizar kasar mai karfin maki 7’8 bisa ma’aunin Richter irinta mafi muni da ta abkawa kasar ta Nepal a cikin shekaru 80 da suka gabata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu