Kerry na jagorantar sasanta rikicin siyasa a Afghanistan
Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry zai yi wata tattaunawa da ‘yan takara biyu, dake sa in sa game da sakanakon zaben shugabancin kasar Afghanistan, da dukkansu ke ikirarin lashewa. Ana fatar tattaunawar da za a yi a birnin Kabul, zata taimaka wajen samar da fahimtar juna, don a rantsar da wanda ya yi nasara a karshen wannan watan na Agusta.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Zargin tafka magudi a zaben na watan Yuli ya jefa Afghanistan cikin halin rashin tabbas, inda Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana fargabar samun rarrabuwar kanu ‘yan kasar, irin wanda aka gani lokacin yakin basasa a shekarar 1990.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu