Isra'ila-Falesdinawa
Rikici tsakanin Palasdinawa da Isra'ila na ci gaba da zafafa
Tashe tashen hankulan da suka faro sakamakon kone wani matashi Bapalasdine, sun fantasama daga gabashin birnin Jerusalen, zuwa garuruwan Larabawan da ke cikin kasar Isra’ila. Wannan na faruwa ne bayan wani gwajin da kwararru suka yi, ya nuna cewa kone matashin aka yi da ranshi.Rahotanni na cewa an kara yawan makaman rokan da ake harbawa daga Gaza zuwa Isra’ila, lamarin da ke sanya fargabar samun sabon rikici da kungiyar Hamas, da ke rike da yankunan na Palasdinawa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: