Isa ga babban shafi
Iraq

Majalisar Dokokin Iraki ta kasa zaben sabon shugaba

A yau talata sabuwar majalisar dokokin kasar Iraki ta soma gudanar da zamanta na farko domin zaben sabon shugabanta, da shugaban kasa da kuma nada sabon firaminista.

Mayakan sa kai a Iraki
Mayakan sa kai a Iraki Reuters/路透社
Talla

To dai jim kadan bayan da ‘yan majalisar suka soma zaman ne aka dage shi sakamakon sabanin da ya kunno kai dangane da wanda za’a zaba a matsayin sabon shugaban Majalisar.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da firaminista Nuri Al-maliki ke neman samun yardar majalisar domin ci gaba da rike matsayinsa karo na uku.

Yanzu haka dai kasar ta Iraki na a cikin halin yakin basasa ne, sakamakon yadda mayakan jihadi suka kwace garuruwa da dama daga hannun dakarun gwamnati, sannan kuma suka sanar da kafa sabuwar daular musulunci a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.