Isa ga babban shafi
Iraq

Mayakan Iraqi sun kashe Jami’an tsaro 22

Dakarun kasar Iraqi sun kaddamar da yaki domin kwato garin Tikrit da ya fada ikon Mayakan da ke yin barazana ga gwamnatin kasar. Rahotanni sun ce Mayakan sun kashe Jami’an tsaro kimanin 22 a wata musayar wuta da suka yi a kusa da Bagadaza a yau Assabar.

Dakarun Iraqi suna fafatawa da Mayakan Sunni da ke neman kawo karshen gwamnatin Shi'a
Dakarun Iraqi suna fafatawa da Mayakan Sunni da ke neman kawo karshen gwamnatin Shi'a REUTERS/Ahmed Saad
Talla

An yi musayar wuta a cikin garin Tikrit tsakanin Mayakan da dakarun Iraqi.

Yanzu haka kuma akwai jiragen yakin Amurka da suka ke shawagi domin kare tawagar kwarrun kasar da suka je ba dakarun Iraqi horo.

Shugaban mabiya Shi’a a Iraqi Ayatollah Ali al Sistani ya yi kira ga ‘Yan siyasar kasar su kafa gwamnatin hadin kai domin kawo karshen rikicin kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.