Isa ga babban shafi
Iraqi

Maliki zai ɗauki mayaƙan sa-kai aikin Ƴan Sanda a Iraqi

Firaministan ƙasar Iraqi Nuri Al-maliki, ya yi alƙawarin samarwa mayaƙan sa-kai da ke mara masa baya a Lardin Anbar ta hanyar ɗaukar su aikin Ɗan sanda bayan sun murƙushe ma su yi wa gwamnatinsa bore. A kwanakin da suka gabata ne masu hamayya da gwamnatin Maliki, suka ƙwace ikon biranen fallujah da Ramadi da ke cikin lardin na Anbar, lamarin da ya yi sanadiyar ɓarkewar fada da kuma tserewar mutane sama da dubu uku daga yankin.

Nouri al-Maliki, Firaministan kasar Iraqi
Nouri al-Maliki, Firaministan kasar Iraqi AFP PHOTO/Jim WATSON
Talla

Sai dai babu wani ƙayyadadden lokaci da gwamnatin Maliki tace zata aiwatar da alƙawalin na ɗaukar mayaƙan aikin Ƴan sanda inda tuni da yawansu suka rungumi makamai domin taimakawa Amurka yaƙi da Mayaƙan al Qaeda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.