Isa ga babban shafi
Palasdinu

Palasdinawa sun yi bukin cika shekaru 46 da yaki da Isra'ila

Hukumomin Palasdinu sun yi bukin cika shekaru 46, da fara yaki da kasar Isra’ila, inda suka nemi a dora duk wata tattaunawa da hukumomin birnin Tel Abiv, kan amincewa da iyakokin kasar ta Palasdinu, kafin mamayar da Yahudawan suka yi a shekarar 1967. Babban mai shiga tsakani na bangeren Palasdinawan Saeb Erakat ya ziyarci kauyuka 3, da mazauna suka tsere, yayin da kasar ta Isra’ila ta mamaye su a yakin da ta shafe kwanaki 6, ana gwabzawa da sojojinn kasashen Misrah Jordan da Siriya.Kasar ta Isra’ila ta mamaye da yammacin kogin Jordan, da kuma gabashin birnin Jerusalem a zamanin yakin, da Palasdinawa suka bayyana a matsayin koma baya garesu.Mr Erakat yace halin da Palasdinawa dubu 5 suka fada a yakin na shekarar 1967, sakamakon fidda su daga kauyukan nasu ne, ke ci gaba da fada musu a yankin yammacin lgin Jordan a wannan zamanin.Ya jaddada bukatar dakatar da gine ginen da Yahudawa ke yi a yankunan Palasdinawa, tare da mika dukka iyakokin da ake da su kafin yakin, a matsayin matakin farko na tattaunawa da Isra’ila.sai dai a nata bangaren, kasar ta Isra’ila ta nemi a ci gaba da tattaunawa ba tare da gindaya wani shardi daga bangaren Palasdinawan ba.A watan Satumban shekarar 2010 wattaunawa tsakanin bangarorin 2 ta ruguje, sakamakon rashin fahimtar juna kan batun na kan iyakoki. 

Babban mai shiga tsakani na Palasdinawa Saeb Erakat
Babban mai shiga tsakani na Palasdinawa Saeb Erakat AFP/Abbas Momani
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.