Pakistan
Harin bam ya kashe mutane 14 a Pakistan
Wani harin bam da aka kai a kasar Pakistan ya hallaka Sojin kasar 14 kana wasu 25 sun jikkata. Wannan harin dai ya auku ne a wani yanki mara isasshen tsaro dake kan iyakar kasar da kasar Afghanistan.
Wallafawa ranar:
Talla
Wannan harin bam din an kai shi ne kan jerin gwanon motocin sojin kasar a kauyen Dosali na Arewacin Waziristan, wani wurin da ‘ya’yan kungiyar Taliban ke tsare dashi.
Jami’an tsaro ne dai suka bada tabbacin mutuwar Sojin 14, wasu 25 kuma rai a hannun Allah.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu