Isa ga babban shafi
Indonesiya

An fara neman gawarwakin wadanda suka mutu a hadarin jirgin Indonesiya

A kasar Indonesia, a yau juma’a masu aikin ceto, dauke da jikkunan zuba gawarwaki sun fara isa zuwa tsaunin nan da jirgin saman kasar Rasha, dauke da mutane 45 ya fadi. Ma’aikatan na anfani da kayan hawan tsauni, don hawa tsaunin Salak, da ke kudancin birnin Jakarta, kuma an ce suna gab da kaiwa inda gawarwakin fasinjojin jirgin suke.Kwamandan sojojin da ke aikin, kanar Anton Mukti Putranto yace wasu daga cikin ma’aikatan nashi suna hawa tsaunin daga kasa yayin da wasu, da suka je kololuwar shi, suke saukowa, inda za su hadu da juna. 

Tsaunin Salak na Indonesiya, da jirgin saman kasar Rasha ya fadi
Tsaunin Salak na Indonesiya, da jirgin saman kasar Rasha ya fadi Reuters
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.