Indiya
wani jirgin ruwa dauke da mutane 250 ya nutse a kasar Indiya
A kasar India wani kwale-kwale dauke da mutane akalla 250 ya nutse a wani kogi, bayan wani mummunar iskar da ya taso, amma anyi katarin ceto mutane akalla 50.Kwale-kwalen mai hawa daya, ya nutse ne cikin kogin Brahma-putra dake jihar Assam, kamar yadda ‘yan sandan wannan yanki suka tabbatar bayan aukuwan hadarin.Yanzu haka dai an tsamo gawawakin mutane sama da 40 a yayin da jami’an agaji ke ta kokarin ceto sauaran jama’ar ko kuma tsamo gawawwakinsu.
Wallafawa ranar: